Kotun majistare mai lamba 58 karkashin mai shari’a, Alkali Aminu Gabari, ya sake bayar da belin tsohon kwamishinan ayyuka, Mu’azu Magaji.
Kotun ta amince da babban limamin Dan Sarauniya ya tsaya wurin fito da Mu’azu Magaji, sai dai kotun ta bukaci ya guje wa duk wata wallafa daga soshiyal midiya har sai an kammala shari’ar, kuma ya biya gilashin motar gidan yari da magoya bayansa suka fasa.
Lauyan wanda ake zargi, Garzali Datti Ahmed, ya mika bukatar sake duba sharuddan belin inda ya yi kira ga kotun da ta duba bukatarsa.
A hukuncin kotun wanda ta bayar da belin Magaji a ranar 4 ga watan Fabrairu, ta saka gindaya wasu sharuddan da za a cika kafin karbarsa.
Daily Trust ta rawaito cewa, kotun ta bada belinsa kan kudi har N1 miliyan da tsayayyu biyu wadanda za su kasance dagacin kauyen Dan Sarauniya da kwamandan Hisbah daga Dawakin Tofa ko kuma babban limami.