Bayan wata hayaniya da aka samu a unguwar Yelwa da ke Bauchi, a lokacin da wasu fusatattun matasa suka mamaye shelkwatar ‘yan sanda ta Yelwa, domin nuna rashin amincewarsu da kisan da wani dan sanda ya yi wa mutane biyu.
An ce dan sandan da ake zargin ya daba wa mutane uku wuka, amma biyu suka mutu nan take.
Lamarin ya haifar da tashin hankali yayin da ’yan bangar suka mamaye tituna, inda suka tare hanyar da ta taso daga mahadar Cocin Elim zuwa hedikwatar shiyya ta Yelwa.
Da take tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta raba wa manema labarai sa’o’i bayan hayaniyar, rundunar ‘yan sandan ta bayyana sunan wanda ake zargin PC Lukman Madaki.
Rahotanni sun bayyana cewa, jami’in na Toro Dibision yana aiki ne a ofishin wasanni, Shelkwatar ‘yan sandan jihar Bauchi.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Ahmed Mohammed Wakil, wanda ya bayyanawa manema labarai cikakken bayanin lamarin a wata sanarwa a ranar Juma’a, 25 ga watan Maris, ya ce, lamarin ya faru ne a wani sintiri a wani bakar fata a Yelwa.