fidelitybank

Dan Sanda ya ki amincewa da karbar miliyan 1 daga masu garkuwa a Kano

Date:

Jami’in ‘yan sandan da ke kula da sashin yaki da masu garkuwa da mutane, sashen binciken manyan laifuka na jihar Kano, SP Aliyu Mohammed, ya ki amincewa da karbar kudi naira miliyan daya (N1,000,000:00) da aka ba shi a matsayin cin hanci domin a sako wani mutum mai shekaru 27.

Wani matashi mai suna Yusuf Ibrahim da ke kauyen Danjibga, karamar hukumar Tsafe, jihar Zamfara.

Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda, SP. Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya tabbatar wa manema labarai hakan a wata sanarwa.

Kiyawa ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Talata lokacin da wani Bamuwa Umaru mai shekaru 62 a garin Shika dake karamar hukumar Sabon Gari a jihar Kaduna ya je wajen jami’in ya ba shi kudi har Naira Miliyan daya (N1,000,000:00) a matsayin cin hanci. domin a sako Yusuf Ibrahim mai shekaru 27, wanda ake zargi da yin garkuwa da mutane.

Jami’an ‘yan sanda sun kama wanda ake zargin mai garkuwa da mutane ne Yusuf Ibrahim bayan daya daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a tashar mota Rijiyar Zaki Kano ta gano shi.

Wanda ake zargin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa kuma yana da hannu dumu-dumu cikin satar mutane a kauyukan Sheme, Yankara, Faskari, da Kucheri dake cikin jihohin Katsina da Zamfara.

Ya ce kungiyarsu ta kashe kusan goma (10) daga cikin wadanda abin ya shafa.

Za a gurfanar da wadanda ake zargin zuwa kotu bayan an kammala bincike.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp