Jami’in ‘yan sandan da ke kula da sashin yaki da masu garkuwa da mutane, sashen binciken manyan laifuka na jihar Kano, SP Aliyu Mohammed, ya ki amincewa da karbar kudi naira miliyan daya (N1,000,000:00) da aka ba shi a matsayin cin hanci domin a sako wani mutum mai shekaru 27.
Wani matashi mai suna Yusuf Ibrahim da ke kauyen Danjibga, karamar hukumar Tsafe, jihar Zamfara.
Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda, SP. Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya tabbatar wa manema labarai hakan a wata sanarwa.
Kiyawa ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Talata lokacin da wani Bamuwa Umaru mai shekaru 62 a garin Shika dake karamar hukumar Sabon Gari a jihar Kaduna ya je wajen jami’in ya ba shi kudi har Naira Miliyan daya (N1,000,000:00) a matsayin cin hanci. domin a sako Yusuf Ibrahim mai shekaru 27, wanda ake zargi da yin garkuwa da mutane.
Jami’an ‘yan sanda sun kama wanda ake zargin mai garkuwa da mutane ne Yusuf Ibrahim bayan daya daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a tashar mota Rijiyar Zaki Kano ta gano shi.
Wanda ake zargin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa kuma yana da hannu dumu-dumu cikin satar mutane a kauyukan Sheme, Yankara, Faskari, da Kucheri dake cikin jihohin Katsina da Zamfara.
Ya ce kungiyarsu ta kashe kusan goma (10) daga cikin wadanda abin ya shafa.
Za a gurfanar da wadanda ake zargin zuwa kotu bayan an kammala bincike.