fidelitybank

Dan Sanda ya ki amincewa da karbar miliyan 1 daga masu garkuwa a Kano

Date:

Jami’in ‘yan sandan da ke kula da sashin yaki da masu garkuwa da mutane, sashen binciken manyan laifuka na jihar Kano, SP Aliyu Mohammed, ya ki amincewa da karbar kudi naira miliyan daya (N1,000,000:00) da aka ba shi a matsayin cin hanci domin a sako wani mutum mai shekaru 27.

Wani matashi mai suna Yusuf Ibrahim da ke kauyen Danjibga, karamar hukumar Tsafe, jihar Zamfara.

Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda, SP. Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya tabbatar wa manema labarai hakan a wata sanarwa.

Kiyawa ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Talata lokacin da wani Bamuwa Umaru mai shekaru 62 a garin Shika dake karamar hukumar Sabon Gari a jihar Kaduna ya je wajen jami’in ya ba shi kudi har Naira Miliyan daya (N1,000,000:00) a matsayin cin hanci. domin a sako Yusuf Ibrahim mai shekaru 27, wanda ake zargi da yin garkuwa da mutane.

Jami’an ‘yan sanda sun kama wanda ake zargin mai garkuwa da mutane ne Yusuf Ibrahim bayan daya daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a tashar mota Rijiyar Zaki Kano ta gano shi.

Wanda ake zargin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa kuma yana da hannu dumu-dumu cikin satar mutane a kauyukan Sheme, Yankara, Faskari, da Kucheri dake cikin jihohin Katsina da Zamfara.

Ya ce kungiyarsu ta kashe kusan goma (10) daga cikin wadanda abin ya shafa.

Za a gurfanar da wadanda ake zargin zuwa kotu bayan an kammala bincike.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...

Bankin Duniya zai kashe wa yankin Arewa a Najeriya dala miliyan 300

Bankin Duniya ya amince da kasafin kuɗi dala miliyan...

Giyar mulki na kwasar Trump – ‘Yan Majalisar Democrat

'Yan Democrats a Amurka sun zargi Donald Trump da...

Kama Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi ba daidai ba ne – PDP

Jam'iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da...

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...
X whatsapp