Hukumar kula da kwallon kafa ta Afrika CAF ta nada wani jamiāin hukumar kwallon kafar kasar Morocco, Hamza El Fariq a matsayin babban alkalin wasa a wasan neman cancantar shiga gasar cin kofin Afrika ta 2024 tsakanin Najeriya da Ghana.
El Fariq zai samu taimakon ‘yan uwansa Abdessamad Abertoune (mataimaki na farko) Zakaria Bouchtaoui (mataimaki na biyu) da Hicham Temsamani (jami’i na hudu).
Yarima Kai Saquee daga Saliyo ne zai zama kwamishinan, yayin da Miboti Moise daga Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo zai kasance a matsayin mai tantance alkalan wasa.
Za a yi karawar ne a filin wasa na Godswill Akpabio International Stadium, Uyo ranar Asabar.
An tashi wasan ne da ci 0-0 a wasan farko na neman tikitin shiga gasar.
Duk masu nasara za su ci gaba zuwa CHAN 2024.