fidelitybank

Dan bindiga ya tarwatsa kansa da abun fashewa

Date:

Wani da ake zargin dan ta’adda ne a unguwar Keke da ke kan titin Ibrahim Haske, a cikin garin Kaduna Millennium City, ya tarwatsa kansa da na’urar fashewa a lokacin da jami’an tsaro suka kama shi, inda ya gagara kaucewa kama shi.

Wata majiya da ta bayyana hakan ga wakilin DAILY POST a ranar Litinin a Kaduna, ta ce jami’an tsaro sun isa gidan wanda ake zargin da karfe 1:00 na safe yayin da unguwar ta farka da karar harbe-harbe.

A cewar majiyar, wanda ake zargin ya budewa jami’an tsaro wuta ne a lokacin da ya gano cewa an kewaye gidansa. Hakan ya kai ga musayar wuta. Bayan da karfin wuta na jami’an tsaro ya rinjaye shi, sai ya yi amfani da bama-bamai ya tarwatsa kansa.

Bayan faruwar lamarin jami’an tsaro sun dira a gidansa inda suka gano bindiga kirar AK-47 tare da wasu bama-bamai guda biyu da jami’an da ke yaki da bama-bamai suka kwance su.

“Bamabaman sun tarwatsa gawar mutumin, yayin da jami’an DSS suka tafi da matarsa da ‘ya’yansa a cikin motocinsu,” inji majiyar.

Wani shugaban al’ummar garin Malam Samaila ya tabbatar da faruwar lamarin.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, DSP Jalige Mohammed, bai amsa sakon tes da aka aike masa ba bayan da ya kasa amsa kiran wayar da aka yi masa.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp