fidelitybank

Dambaruwar Sarkin Kano: Kotu ta sanya ranar 13 a kan bayyana hukunci

Date:

Babbar kotun tarayya da ke Kano ta sanya ranar 13 ga watan nan na Yuni domin bayyana hukuncinta a kan ko tana da hurumin sauraron ƙarar da aka shigar gabanta kan rushe masarautu biyar a jihar ko kuma ba ta da hurumi.

Tun da farko kotun ta bukaci bangarorin biyu su yi mata bayani kan ko tana da hurumin ko kuma a’a inda kowanne bangare ya yi bayani tare da kafa hujjoji da irin shari’o’in da suka gabata kan rikicin masarautu a ƙasar.

Lauyan ɓangaren gwamnatin Kano ya shaida wa kotun cewa wanda ya shigar da karar ma ba shi da hurumin neman kare masa hakki saboda dokar da ta ba shi damar zama ɗan majalisar sarki an rushe ta.

To amma lauyan mai ƙara ya ƙalubalanci hakan da cewa, idan ana batu na take haƙƙin ɗan’Adam to al’amari ne da ba shi da iyaka don haka kotun ta ci gaba da sauraron wannan Shari’a.

Bayan sauraren doguwar mahawarar daga dukkanin ɓangarori biyun alƙalin kotun AM Liman, ya sanar da ranar da kotun za ta yanke hukunci kan wannan batu.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp