Kotun da ke shiga tsakanin ma’aikata da wadanda suka dauke su aiki ta dage wata kara da gwamnatin Najeriya ta shigar kan yajin aikin da kungiyar malaman ta shafe watanni tana yi.
Alkalin kotun P.I. Hamman ne ya dage sauraren shari’ar zuwa 16 ga watan Satumba bayan da wata kungiya mai fafutukar kare hakkin dan Adam ta mika bukatar yin haka ga alkalin.
Ita ma kungiyar ta shigar da wata kara mai kama da wadda gwamnatin Najeriya ta shigar, lamarin da ya sa alkalin ya dage karar domin a warware matsalar kafin ta zama karfen kafa ga shari’ar.
Sai dai lauyan da ke wakiltar gwmnati Tijjani Gazali (SAN) ya ki amincewa da bukatar a hada kararrakin biyu wuri guda, yana cewa lokacin yin haka bai yi ba.
Amma lauyan ASUU Femi Falana (SAN) ya sanar da manema labarai cewa a sane yake da bukatar da aka gabatar wa kotun na hade kararrakin wuri guda.