Sabon dan wasan Everton Dele Alli ya ce, damar da Frank Lampard zai ba shi domin ya taka leda, ya sanya komawar sa Everton.
An nada Lampard a matsayin kociyan Toffees ne a ranar karshe na rufe cinikin ‘yan wasa kuma ya sanya Alli a gaba, inda ya dauko shi daga Tottenham kan kudi da zai kai fam miliyan 40.
Alli, mai shekaru 25, ya yi kokawa wajen ganin ya fi kyau a kwanan nan kuma ya buga wasanni 10 kacal a gasar Premier bana.
“Ina nan kuma ina neman in nuna abin da zan iya yi, kuma in nuna wa kowa mafi kyawun ni ne Dele,” in ji shi.