fidelitybank

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Date:

Mataimakin shugaban jam’iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar Dalori ya maye gurbin Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar na riƙo.

Wannan na zuwa ne bayan tsohon gwamnan na jihar Kano ya ajiye muƙamin a ranar Juma’a, sannan aka naɗa Dokta Ali Bukar Dalori a matsayin wanda zai riƙe muƙamin, kafin a kai ga zaɓen wanda zai maye gurbinsa.

Mutane dai sun yi zargin ruwa ba ya tsami banza, ko kuma dai da walakin goro a miya amma uwar jam’iyyar ta yi watsi da wannan hasashe.

Bala Ibrahim shi ne daraktan yaɗa labarai na jam’iyyar ta APC, ya ce “Game da batun wanda zai maye gurbin shugaban jam’iyyar da sauka, dama jam’iyya na da kundin tsarin mulki wanda ya yi tanadi irin wannan wanda idan shugaban jam’iyya ya sauka daga muƙaminsa to za a zaɓi ɗaya daga cikin mataimakansa biyu wanda ɗaya daga arewa ɗaya kuma daga kudu to sai a ba wanda ya fito daga yankin da shugaban da ya yi murabus ya fito a bashi riƙon ƙwarya kafin a gudanar da zaɓen wanda zai gaji kujerar.”

Ya ce,” A wannan hali muƙaddashi na arewa tun da Ganduje daga shiyyar ya fito wanda shi ne Bukar Dalori, shi ne zai rike kujerar na wucin gadi har lokacin da aka zabi sabon shugaban jam’iyyar.”

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...
X whatsapp