fidelitybank

Dalilin da yasa Likitoci masu neman kwarewa suka janye yajin aiki

Date:

Kungiyar likitoci masu neman kwarewa ta kasa, ta koma bakin aiki bayan yajin aikin gargadi da mambobinta da ke aiki a asibitocin gwamnati suka yi na kwana biyar.

Sanarwar da shugabanta ya fitar ta ce matakin ya biyo bayan sake nazarin alkawuran da gwamnati ta yi ne a ganawar da suka yi tsakaninsu ta karshe.

Daga cikin bukatun kungiyar akwai neman kara wa likitocin masu neman kwarewa albashi kashi dari biyu cikin dari da daukar sabbin likitocin da za su maye gurbin wadanda suka bar aiki da kuma samar da kayan aiki da ake bukata a asibitocin gwamnati.

Haka kuma likitocin na neman a janye kudurin dokar da aka gabatar kwanannan na neman hana sabbin likitoci barin Najeriya har sai sun yi shekara biyar da aiki a kasar

Shugaban kungiyar likitocin Dr. Emeka Orji ya gaya wa BBC cewa gwamnati ta yi musu alkawarin biyansu wasu kudade a wata mai zuwa.

Ganin cewa wa’adin gwamnatin Buhari zai kare a ranar 29 ga watan nan na Mayu, shugaban ya ce wannan ba wani abu ba ne domin gwamnati za ta ci gaba.

Ya ce in dai har aka biya musu wasu daga cikin bukatunsu a yanzu sabuwar gwamnatin da za ta hau sai ta ji da sauran bukatun nasu.

Likitocin sun ce za su duba su ga yadda al’amura za su kasance nan da mako biyu kafin su yanke shawarar matakin da za su sake dauka.

Dubban likitoci ne suka bar kasar zuwa wasu kasashen na duniya domin aiki saboda korafin rashin wadataccen albashi da yanayin aiki mai kyau.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp