fidelitybank

Dalilin da ya sanya muka rufe gidan caca a Anambra – Soludo

Date:

Gwamnatin jihar Anambra ta yi karin haske kan dalilan da suka sa ta dakatar da duk wasu wuraren caca a otal-otal da gidajen abinci da mashaya a jihar.

Gwamnatin ta ce, dakatarwar ya zama dole ne biyo bayan wasu ayyukan damfara da ake zargin ana tafkawa a cibiyoyin, inda ta kara da cewa ba ta hana ayyukan Bet9ja da sauran kayan caca a jihar ba.

Hakan ya fito ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kwamishinoni uku na al’adu, nishaɗi da yawon bude ido, harkokin cikin gida, da shugaban hukumar tattara kudaden shiga na jihar Anambra, Don Onyenji, Chikodi Anara, da Richard Madiebo, bi da bi.

Sanarwar ta zargi masu gudanar da na’urorin wasannin gidan caca da masu otal-otal da mashaya da rashin nuna gaskiya wajen biyan kudaden da aka ci wasan, wanda ta ce babban cin zarafi ne.

Sanarwar ta kara da cewa: “Ma’aikatar Al’adu, Nishadi da Yawon shakatawa na karbar koke-koke da dama na magudin injinan wasan gidan caca da kuma rashin nuna gaskiya wajen biyan kudi don cin wasan wanda babban cin zarafi ne na kyawawan ayyuka na duniya.

“Saboda haka, ma’aikatar yawon bude ido tare da hadin gwiwar hukumar tattara kudaden shiga ta jihar Anambra, AIRS da ma’aikatar harkokin cikin gida suna ba da umarnin masu gudanar da wasannin caca a otal-otal, gidajen cin abinci da mashaya da su dakatar da duk ayyukan wasan caca da gidan caca tare da samun sakamako nan take har sai an kammala bincike. .”

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp