fidelitybank

Dalilin da ya sanya mu ka nada Yusuf Buhari – Sarkin Daura

Date:

Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Farouk, ya bayyana ainihin dalilin da ya sa ya baiwa Yusuf Buhari sarauta a masarautar Daura.

Yusuf dai, wanda shi kadai ne dan shugaban kasa, Muhammadu Buhari, za a nada shi sarautar, Talban Daura, kuma hakimin Kwasarawa ranar Asabar mai zuwa.

Sarkin na jawabi ne a fadarsa ranar Alhamis, yayin bikin nadin sarautar wasu Dagatai guda Hudu a masarautar.

A cewarsa, sarautar za ta hana Yusuf din yin sintiri tsakanin Abuja da Yola garin mahaifiyarsa, alhali Daura ne asalin garinsa.

“Mun ba shi sarautar nan ne, saboda saka irin alhairan da shugaba Buhari ya kawo Daura a matsayin mahaifarsa. Ko ba ka kaunar Buhari, ka san Daura a yau ta ci gaba fiye da shekarun baya. Saboda mu saka masa, mun ba shi sarautar Talban Daura, wanda shi kuma ya ba babban dansa, Yusuf. Hakan zai hana shi sintiri tsakanin Abuja da Yola in mahaifinsa ya bar mulki.

“Mun samu Jami’ar Sufuri da Kwalejin Fasaha da tituna kusan a kowane layi a Daura. A zahirin gaskiya a yau, Daura ta fi wasu Jihohin na Najeriya ma ci gaba. Muna da ’ya’yan Daura da yawa da suka yi fice amma ba sa son alakanta kansu da ita, amma Buhari ya ciri tuta a nan bangaren,” inji Sarkin.

Daga cikin sabbin Dagatan da aka nada har da Armaya’u Bello, wanda aka ba Dagacin Fatautawa, kuma Sarkin Gabas Kwasarawa. A cewar Aminiya.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp