fidelitybank

Dalilin da ya sanya mu ka nada Yusuf Buhari – Sarkin Daura

Date:

Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Farouk, ya bayyana ainihin dalilin da ya sa ya baiwa Yusuf Buhari sarauta a masarautar Daura.

Yusuf dai, wanda shi kadai ne dan shugaban kasa, Muhammadu Buhari, za a nada shi sarautar, Talban Daura, kuma hakimin Kwasarawa ranar Asabar mai zuwa.

Sarkin na jawabi ne a fadarsa ranar Alhamis, yayin bikin nadin sarautar wasu Dagatai guda Hudu a masarautar.

A cewarsa, sarautar za ta hana Yusuf din yin sintiri tsakanin Abuja da Yola garin mahaifiyarsa, alhali Daura ne asalin garinsa.

“Mun ba shi sarautar nan ne, saboda saka irin alhairan da shugaba Buhari ya kawo Daura a matsayin mahaifarsa. Ko ba ka kaunar Buhari, ka san Daura a yau ta ci gaba fiye da shekarun baya. Saboda mu saka masa, mun ba shi sarautar Talban Daura, wanda shi kuma ya ba babban dansa, Yusuf. Hakan zai hana shi sintiri tsakanin Abuja da Yola in mahaifinsa ya bar mulki.

“Mun samu Jami’ar Sufuri da Kwalejin Fasaha da tituna kusan a kowane layi a Daura. A zahirin gaskiya a yau, Daura ta fi wasu Jihohin na Najeriya ma ci gaba. Muna da ’ya’yan Daura da yawa da suka yi fice amma ba sa son alakanta kansu da ita, amma Buhari ya ciri tuta a nan bangaren,” inji Sarkin.

Daga cikin sabbin Dagatan da aka nada har da Armaya’u Bello, wanda aka ba Dagacin Fatautawa, kuma Sarkin Gabas Kwasarawa. A cewar Aminiya.

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp