fidelitybank

Dalilin da ya sanya kotu ta dakatar da Ganduje daga mukaminsa

Date:

Wata babbar kotu a jihar Kano ta dakatar da Dakta Abdullahi Umar Ganduje da ga shugabancin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya.

Mai shari’a Usman Malam Na’abba ne ya yanke hukuncin bayan ƙarar da Dakta Ibrahim Sa’ad ya shigar a madadin jagororin jam’iyyar biyu a mazaɓar Ganduje da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a Kano.

Mambobin jam’iyyar da aka shigar da ƙarar a madadinsu su ne – mataimakin sakatare, Laminu Sani da mai bai wa APC shawara kan harkokin shari’a, Haladu Gwanjo waɗanda suke cikin ƴan jam’iyyar tara da suka dakatar da Ganduje kwanaki biyu da suka gabata.

Kotun ta kuma nemi Ganduje da ya daina ayyana kansa a matsayin mamba a jam’iyyar ta APC.

Mai shari’a Na’abba ya dakatar da kwamitin gudanarwar jam’iyyar APC a Kano da ya guji yin katsalandan kan matakin shugabannin jam’iyyar a mazaɓar Ganduje da kashi biyu bisa uku na galibin shugabannin jam’iyyar suka sa hannu a kai kamar yadda kundin tsarin jam’iyyar ya tanada.

A baya-bayan nan ne wasu shugabannin APC tara a mazaɓar ta Ganduje suka ce sun ɗauki matakin dakatar da Ganduje bayan wata takardar koke da wani ɗan jam’iyyar Ja’afaru Adamu ya shigar.

A takardar koken, Adamu ya yi magana kan tuhume-tuhumen rashawa da ake yi wa tsohon gwamnan inda ya buƙaci jagororin mazaɓar su gudanar da bincike kan batun domin farfaɗo da ƙimar jam’iyyar da kuma tasirin da batun zai yi a fafutukar gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta yaƙi da rashawa.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...
X whatsapp