fidelitybank

Dalilin da ya sanya kotu ta dakatar da Ganduje daga mukaminsa

Date:

Wata babbar kotu a jihar Kano ta dakatar da Dakta Abdullahi Umar Ganduje da ga shugabancin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya.

Mai shari’a Usman Malam Na’abba ne ya yanke hukuncin bayan ƙarar da Dakta Ibrahim Sa’ad ya shigar a madadin jagororin jam’iyyar biyu a mazaɓar Ganduje da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a Kano.

Mambobin jam’iyyar da aka shigar da ƙarar a madadinsu su ne – mataimakin sakatare, Laminu Sani da mai bai wa APC shawara kan harkokin shari’a, Haladu Gwanjo waɗanda suke cikin ƴan jam’iyyar tara da suka dakatar da Ganduje kwanaki biyu da suka gabata.

Kotun ta kuma nemi Ganduje da ya daina ayyana kansa a matsayin mamba a jam’iyyar ta APC.

Mai shari’a Na’abba ya dakatar da kwamitin gudanarwar jam’iyyar APC a Kano da ya guji yin katsalandan kan matakin shugabannin jam’iyyar a mazaɓar Ganduje da kashi biyu bisa uku na galibin shugabannin jam’iyyar suka sa hannu a kai kamar yadda kundin tsarin jam’iyyar ya tanada.

A baya-bayan nan ne wasu shugabannin APC tara a mazaɓar ta Ganduje suka ce sun ɗauki matakin dakatar da Ganduje bayan wata takardar koke da wani ɗan jam’iyyar Ja’afaru Adamu ya shigar.

A takardar koken, Adamu ya yi magana kan tuhume-tuhumen rashawa da ake yi wa tsohon gwamnan inda ya buƙaci jagororin mazaɓar su gudanar da bincike kan batun domin farfaɗo da ƙimar jam’iyyar da kuma tasirin da batun zai yi a fafutukar gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta yaƙi da rashawa.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp