fidelitybank

Dalilin da ya sa Ƴansanda ba za su taya EFCC kama Yahaya Bello ba – Fadar Shugaban Ƙasa

Date:

Kakakin shugaban Najeriya, Bayo Onanuga ya ce jami’an tsaron Najeriya ba su da damar kama tsohon gwamnan Kogi Yahaya Bello saboda ”sarƙaƙiyar” da ke tattare da shari’ar da ake yi masa.

Yayin da yake hira da gidan Talbijin na Channels ta cikin shirin ‘ Inside Sources’ a ranar Lahadi, Mista Onanuga ya ce Yahaya Bello na ɓoye ne a gidan gwamnan jihar Kogi wanda shi kuma kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba shi kariya.

A watan Afrilun da ya gabata ne hukumar EFCC, mai yaƙi da cin hanci da almundahanar kuɗaɗe ta Najeriya, ta ayyana neman tsohon gwamnan ruwa a jallo, saboda zargin laifukan badaƙalar kuɗi da suka kai naira biliyan 80.2

Jami’an hukumar EFCC sun taɓa mamaye gidan Yahaya Bello a yunƙurin kama shi, to amma sai sai aka yi zargin cewa gwamnan jihar wanda ya gaje shi, Usman Ododo ya je gidan domin tseratar da shi zuwa gidansa, kamar yadda gidan talbijin na Channels ya ruwaito.

”To wannan shi ne dalilin” a cewar bayo Onanuga, ”saboda matsalar ita ce idan dai Yahaya Bello na gidan gwamna Ododo, to ‘yansanda ba za su iya kama shi ba, saboda yin hakan ya saɓa wa kariyar da gwamnan ke da ita”.

”Usman Ododo na da kariya, kuma ana ganin Yahaya Bello na ɓoye a gidansa, don haka ‘yansanda ba za su iya zuwa gidan domin kama wani ba”.

”Batun yana da sarƙaƙiya, EFCC a matsayinta na hukumar gwamnatin tarayya, ba za ta iya kama shi ba idan yana cikin gidan gwamnan da yake da kariya daga tuhuma ko kamu”, in Onanuga.

Yahaya Bello ya riƙe muƙamin gwamnan jihar Kogi na tsawon wa’adi biyu.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...
X whatsapp