Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Adamu, ya bayyana dalilin da ya sa ake daukar lokaci mai tsawo kafin shugaba Bola Tinubu ya bayyana sabbin ministocinsa.
Da yake magana a ranar Litinin a Abuja, yayin ganawarsa da shugabannin jam’iyyar APC a fadin kasar nan, Adamu ya bayyana cewa Tinubu ya yi tuntubar juna sosai kafin ya yanke shawarar sunayen da zai zaba.
“Shugaban kasa ya fara. Kuma yana yawan tuntubar sa kafin ya fito da wadanda ya nada a matsayin ministoci.
“Nadin ministocin zai zo farko. Za su yi ta tantance su har sai an bayyana su bayan an gabatar da su daga hannun maigirma shugaban kasa.
“Kuma mai girma shugaban kasa zai nada ministocinsa a hukumance ya rantsar da su.
“Bayan ya yi hakan ne zai bayyana kowannen su ga kasar don sanin ministar da zai je wace ma’aikatar, da kuma ma’aikatu nawa ne za mu samu,” in ji Adamau.