fidelitybank

Dalilin da ya sa shugaban jam’iyyar APC da mataimakin sa suka jingine kujerar su ta Majalisa

Date:

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, a ranar Talata, ya yi murabus daga mukaminsa na Sanata mai wakiltar Nasarawa ta Yamma a majalisar dattawa ta 9.

Hakan ya faru ne yayin da sabon zababben mataimakin shugaban jam’iyyar yankin (Arewa), Abubakar Kyari, shi ma ya yi murabus a matsayin dan majalisa mai wakiltar Borno ta Arewa.

Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ne ya karanta wasikun murabus din na ‘yan majalisar biyu yayin zaman majalisar.

Sanata Abdullahi Adamu, har zuwa lokacin da aka zabe shi a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasa, ya shugabanci kwamitin noma da raya karkara.

Shi kuwa Kyari shi ne shugaban kwamitin kula da babban birnin tarayya (FCT).

Wasikar Sanata Adamu ta ce, “Cikin girmamawa da godiya nake sanar da ku cewa sakamakon nasarar da na samu a matsayina na shugaban kasa a babban taron jam’iyyarmu ta APC da aka kammala a ranar 26 ga Maris, 2022. A yau na yi murabus a matsayin Sanatan Tarayyar Najeriya mai wakiltar Nasarawa ta Yamma daga ranar 1 ga Afrilu, 2022.

“Aikin murabus na zai bar ni da cikakken tuna irin hadin kai da zumuncin da kuka iya yi tsawon shekaru goma sha daya da na yi a Majalisar Dattawa.

“Ina isar da sakona ga dukkan takwarorina cewa su ba da lokaci wajen hada kai da mu a shelkwatar jam’iyyar mu ta APC, domin yin abin da ya dace a kokarinmu na isar da zaben shugaban kasa da na kasa a 2023 ga jam’iyyarmu da mabiyanta.

“Ina kuma rokon ku mika godiyata ga dukkan abokan aikinmu da ma’aikatan majalisar.”

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar Ĉ™asar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun Ĉ™addamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buĈ™atu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa Ĉ™uri’a domin yanke hulɗa...
X whatsapp