Shugaban jamâiyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, a ranar Talata, ya yi murabus daga mukaminsa na Sanata mai wakiltar Nasarawa ta Yamma a majalisar dattawa ta 9.
Hakan ya faru ne yayin da sabon zababben mataimakin shugaban jam’iyyar yankin (Arewa), Abubakar Kyari, shi ma ya yi murabus a matsayin dan majalisa mai wakiltar Borno ta Arewa.
Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ne ya karanta wasikun murabus din na âyan majalisar biyu yayin zaman majalisar.
Sanata Abdullahi Adamu, har zuwa lokacin da aka zabe shi a matsayin shugaban jamâiyyar APC na kasa, ya shugabanci kwamitin noma da raya karkara.
Shi kuwa Kyari shi ne shugaban kwamitin kula da babban birnin tarayya (FCT).
Wasikar Sanata Adamu ta ce, âCikin girmamawa da godiya nake sanar da ku cewa sakamakon nasarar da na samu a matsayina na shugaban kasa a babban taron jamâiyyarmu ta APC da aka kammala a ranar 26 ga Maris, 2022. A yau na yi murabus a matsayin Sanatan Tarayyar Najeriya mai wakiltar Nasarawa ta Yamma daga ranar 1 ga Afrilu, 2022.
âAikin murabus na zai bar ni da cikakken tuna irin hadin kai da zumuncin da kuka iya yi tsawon shekaru goma sha daya da na yi a Majalisar Dattawa.
âIna isar da sakona ga dukkan takwarorina cewa su ba da lokaci wajen hada kai da mu a shelkwatar jamâiyyar mu ta APC, domin yin abin da ya dace a kokarinmu na isar da zaben shugaban kasa da na kasa a 2023 ga jamâiyyarmu da mabiyanta.
“Ina kuma rokon ku mika godiyata ga dukkan abokan aikinmu da ma’aikatan majalisar.”