fidelitybank

Dalilin da ya sa Ronaldo ya fashe da kuka a Qatar – ‘Yar uwarsa

Date:

‘Yar’uwar Cristiano Ronaldo, Elma Aveiro, ta mayar da martani ga faifan bidiyo na dan uwanta yana kuka, bayan fitar da Portugal daga gasar cin kofin duniya ta FIFA a Qatar 2022.

Ronaldo ya barke da kuka bayan da Morocco ta fitar da Portugal daga gasar cin kofin duniya a karshen mako.

An ga tsohon dan wasan na Manchester United yana kuka a lokacin da ya sauka a rami bayan busar da aka yi na karshe na wasan.

Dan wasan mai shekaru 37, ya fito ne daga kan benci yayin da Morocco ta doke Portugal da ci 1-0 a wasan daf da na kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya bayan Youssef En-Nesyri ya ci kwallo daya tilo a wasan.

Daga nan sai Ronaldo ya bar filin wasa yana kuka a lokacin da Morocco ta fitar da su daga gasar cin kofin duniya ta 2022.

Da take mayar da martani, Aveiro, a wani sako da ta wallafa a shafinta na Instagram a ranar Litinin, ta ce faifan bidiyon Ronaldo na kuka yana da kyau kuma ba za ta gaji da kallonsa ba.

“Kyakkyawan hoto, soyayya, godiya, kima, dabi’u ne da ba kowa ke da shi ba… Yana da kyau wannan bidiyon da ban gaji da kallo ba kuma ba Portuguese ba ne, ban sani ba ko na sanya kaina fahimtar girman kai, babban mutum kasancewarsa, babban ɗa, ɗan’uwa, uba, abin koyi ga kowa da kowa.

“Na gode wa Allah da ya ba ni a matsayina na ɗan’uwa wannan yaro/mutumin da nake alfahari da shi da ƙauna da dukkan ƙarfina. Godiya ga Allah. Na gode, Ronaldo, ” Ta buga tare da bidiyon.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...
X whatsapp