Kimanin watanni biyu da gudanar da zaben shugaban kasa, Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas ya bayyana dalilin da ya sa ya rufe ofishin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku/Okowa a Fatakwal.
Wike ya ce ya rufe ofishin yakin neman zaben ne saboda an kafa shi a Fatakwal ba tare da amincewar gwamnati ba.
Gwamnan ya ce ya yi amfani da umarnin zartarwa na 21 da 22 don ba da goyon bayan doka ga rufe ofishin yakin neman zaben.
Ya bayyana hakan ne a wajen kaddamar da titin Bori-Kono mai tsawon kilomita 17.2 a unguwar Baen da ke karamar hukumar Khana ta jihar.
A cewarsa, “Kwanaki da suka gabata, Maeba da Abiye sun je titin Igboukwu, D-Line (Port Harcourt) ba tare da amincewar gwamnati ba wajen kafa ofishin siyasa.
“Muna magana ne game da Dokokin Zartarwa na 21 da 22 wadanda a yanzu dokar da Majalisar Dokoki ta Jiha ta karbe. Ba mu tura shugaban karamar hukumar Fatakwal ya je ya ruguje shi (ginin) ba. Muna da iko.”
Jam’iyyar PDP ta fada cikin rikicin cikin gida sakamakon gazawar shugaban jam’iyyar na kasa, Iyorchia Ayu, ya yi murabus daga mukaminsa domin share fage ga dan kudu.
Wike ya fusata da shugabancin jam’iyyar PDP saboda yadda ake karkatar da muhimman mukamai a jam’iyyar.
PDP ta ware tikitin takarar shugaban kasa da shugaban jam’iyyar zuwa Arewa, yayin da ta mayar da yankin Kudancin kasar baya.
Don haka, Wike da kungiyar masu fafutukar ganin an tsige Ayu a matsayin Shugaban PDP na kasa.