Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal, ya bayyana dalilin da ya sa ya janye wa Atiku Abubakar a zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar PDP.
Gwamnan, ya ce, wannan sadaukarwa ce ga Nijeriya a matsayin kasa da kuma ‘yan Nijeriya a matsayin al’umma.
Tambuwal, a wajen taron a ranar Asabar din da ta gabata, ya fice daga takarar tare da neman magoya bayansa da su zabi Atiku.
Da yake janyewa daga takarar, Tambuwal ya ce, “Wadanda suke wakilai a nan su zabi Alhaji Atiku Abubakar”.
Gwamnan ya bayyana dalilinsa na murabus ne a lokacin da yake jawabi ga jama’ar da suka yi masa tarba ta jarumtaka a ranar Juma’a bayan ya taso daga Abuja.