fidelitybank

Dalilin da ya sa na dawo APC – Sanata Shehu Sani

Date:

Tsohon dan majalisar dattawa mai wakiltar Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya bayyana dalilin da ya sa ya koma jam’iyyar All Progressives Congress (APC), bayan ficewa daga jam’iyyar PDP.

Sani ya fice daga jam’iyyar APC ne a watan Oktoban 2018 a yayin da ake ta cece-kuce kan zaben fidda gwani na jam’iyyar.

Daga nan sai ya sauya sheka zuwa PDP ya samu tikitin takarar sanata na jam’iyyar. Amma ya sha kaye a zaben 2019 a hannun gwamnan jihar Kaduna mai ci Uba Sani.

A ranar 16 ga Fabrairu, Sani ya koma APC tare da wasu ‘yan PDP da ‘yan jam’iyyar New Nigeria Peoples Party a Kaduna.

Da yake magana a ranar Juma’a a wani shiri na gidan Talabijin na Channels, Hard Copy, Sani ya ce Gwamnan Kaduna ne ke da alhakin komawar sa jam’iyya mai mulki bayan tattaunawar sulhu a fadin jihar.

Ya ce, “Wani al’amari ne ya sa muka fice daga jam’iyyar APC a wani lokaci a shekarar 2018, kuma lamarin ya sauya, daga nan muka koma APC a jihar Kaduna.

“Da farko ni dan jam’iyyar APC ne, musamman a jihar Kaduna. Mun kafa tsare-tsare, kuma mun yi yakin neman zabe, muka ci zaben 2015 a matakin majalisar dattawa da na gwamna, wani waje kuma muka rabu da gwamna (Nasir El-Rufai) a jihar.

“Mun rabu kan bambance-bambancen da suka shafi siyasa, na kashin kai da ma al’amuran da suka shafi jihar, kuma a dalilin haka ne muka kori kanmu daga jam’iyyar, sannan kuma muka samu sabon gwamna da ya kai mu.

“Gwamnan da yake tuntuba, yana gina gadoji a fadin jihar sannan kuma muka hadu muka amince cewa mu koma jam’iyyar da muka kafa a jihar Kaduna.”

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp