fidelitybank

Dalilin da ya sa muka tsunduma yajin aiki – Ma’aikatan Jiragen sama

Date:

Kungiyoyin ma’aikatan sufurin jiragen sama sun fara yajin aikin gargaɗi na kwanaki biyu, domin matsa ƙaimi ga buƙatunsu na kyautata jin daɗin mambobinsu.

Ma’aikatan sun ce, dole ne hukumomin sufuri na jirgin sama guda huɗu su yi aiki da yarjejeniyar da suka kulla tun a shekara ta 2019 wanda har zuwa yanzu ba a aiwatar ba.

Tun da sanyin safiya ne mambobin ƙungiyar suka tare hanyoyin shiga da fita na dukkan sassan da ke kai wa ga hukumar kula da sufurin jiragen sama.

Lamarin ya janyo cikas ga harkokin sufurin, inda suka cire tutocin ‘yan ƙwadago a sama tare da rera waƙoƙin da suka yi ta zaburar da su domin matsa wa hukumomi lamba, su biya musu buƙatunsu da aka cimma. In ji BBC.

Shugabannin ƙungiyar sun ce yajin aikin na ƙasa baki-ɗaya ne kuma ya shafi kowanne sashe na harkokin jiragen sama a ƙasar.

Harkokin da suka shafi sufurin jiragen sama sun fuskanci tsaiko, inda aka dakatar da ayyukansu, yayin da fasinjoji kuma suka rasa damar shiga filayen jirgi.

An samu cunkoson ababen hawa a kewayen harabar filin jirgin sama na Legas sakamakon toshe hanyoyin shiga da fita.

Yajin aiki

Da yawa daga cikin fasinjoji da suka shirya tafiya hankalinsu ya tashi wanda ya zama dole suka ɗauki hayar masu babura da aka haramta ayyukansu a jihar, domin kai isa filin jirgin saman, yayin da wasu kuwa suka yi ta tattaki.

Duk wata hanyar shiga tashar jirgin kama daga Ikeja ƘarƘashin gada da titin Agege da Oshodi da kuma hanyar shiga filin jirgin, sun yi cikar kwari da motoci, yayin da ƙungiyoyin ƙwadago suka taru domin yi wa ma’aikata jawabi kan muradunsu.

Cikin bukatun da ƙungiyar ke neman a biya mata, har da abin da ya shafi aiwatar da gyara kan mafi ƙarancin albashi na hukumar kula da yanayi ta Najeriya, NiMet tun daga 2019.

Yajin aiki

Rahotanni sun ce wakilan gwamnati kan harkokin sufurin jiragen sama sun kira haɗaɗɗiyar kungiyar domin cimma matsaya tare da dakatar da yajin aikin don kar ya haifar da cikas ga masu tafiye-tafiye.

Sai dai shugabannin ƙungiyoyin sun ce ba za su halarci duk wani zama da wakilan gwamnati ba, face bukatarsu ta biya ba.

Kungiyoyin sun sha alwashin ci gaba da yajin aiki na gargaɗi har zuwa gobe ko kuma lokacin da wakilan hukumomin sufurin jiragen saman suka amince da bukatunsu.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp