Gwamnatin Ribas ta sanar da matakin da ta ɗauka na rusawa da sake gina zauren majalisar dokokin jihar, sakamakon matsalolin da wasu ɓangarorin ginin suka fuskanta sanaiyyar fashewar wani abu da kuma tashin gobarar da ta faru a baya-bayan nan, lamarin da ya tilasta sabunta ginin don tabbatar da ingancinsa.
Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Ribas, Joseph Johnson ne ya fitar da wannan sanarwa.
“Bayan tantance ingancin ginin, masana sun shawarci gwamnati cewa ci gaba da amfani da ginin a halin da take ciki zai zama haɗari,” in ji shi.
Johnson ya bayyana ƙoƙarin da gwamnati ke yi na gano matakan bin hanyoyin rage kashe kuɗi wajen gyara har sai sun amince da tsarin sabon ginin.
Kafin lokacin, gwamnatin Ribas ta samar da madadin wurin da majalisar za ta gudanar da harkokinta har sai an sake gina majalisar.” kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Sanarwar ta ce madadin wurin da aka samar don gudanar da harkokin majalisar na wucin gadi yana cikin fadar gwamnati.