Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima wanda ya wakilci shugaba Tinubu, a yayin jawabi a taron Majalisar Ɗinkin Duniya, ya nemi da a yafewa Najeriya da sauran ƙasashe masu tasowa basukan da ake bin su.
“Dole ne mu tabbatar cewa duk wani gyara da za a yi wa tsarin kuɗaɗe na duniya da suka haɗa da cikakken tsarin yafe bashi…domin ƙasashe ƙanana da masu tasowa ba za su iya samun cikakken cigaban tattalin arziƙi ba ba tare da yin duba da sake nazari kan irin nauyin bashin da ke kansu.” In ji Kashim Shettima.
Sauran batutuwan da mataimakin shugaban ya taɓo a jawabin nasa sun haɗa da neman haɗin kan Majalisar Ɗinkin Duniya wajen ganin an mayar da kuɗaɗen sata da waɗanda aka fitar da su zuwa manyan ƙasashe ba bisa ƙa’ida ga ƙasashen da aka sato su.
Sanata Kashim Shettima ya kuma nemi zauren Majalisar da ya bai wa nahiyar Afirka da Najeriya gurbi a kwamitin tsaro na Majalisar ta Ɗinkin Duniya