Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya bayyana dalilan da suka sa suka sha kashi a hannun Manchester United da ci 2-1 a gasar Premier ranar Asabar.
Jack Grealish ya fito daga benci ne ya fara zura kwallo a raga a Old Trafford.
Sai dai masu masaukin bakin sun fafata ne ta hannun Bruno Fernandes da Marcus Rashford inda suka dauki dukkan maki uku.
United yanzu maki daya ne kacal a bayan City kuma tara a bayan Arsenal wadda ke kan gaba.
“Wasan yayi kyau kwarai da gaske. Mun taka rawar gani. Suna da ban mamaki a cikin canje-canje. Taya murna ga tawagar.
“Ina alfaharin zuwa nan in yi wasa da wannan hali. Sun hukunta mu a canje-canje.”
“Mun rasa ‘yar barazana a gaba, dan katse. Muna yin wasa mai ban mamaki, “in ji Guardiola.