fidelitybank

Dalilin da ya sa muka bayar da belin Doguwa – Baba Jibo

Date:

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke jihar Kano, ta bayar da belin Alhassan Ado Duguwa.

Kakakin kotunan Kano, Baba Jibo Ibrahim, ya ce, hakan ya dace da tsarin shari’a, amma za a ci gaba da sauraron shari’ar zargin kisan kai da ake yi masa.

Ya ce Kotun ta kalubalanci rundunar ‘yan sanda saboda kai Alhassan Doguwa gabanta saboda ba ta da hurumin sauraron irin laifin da ake tuhumarsa da shi.

Yan sandan dai na kuma zargin sa da hannu a harbin wasu mutane da bindiga kwana É—aya bayan kammala jefa Æ™uri’a a mazaÉ“arsa ta Doguwa/Tudun wada a zaÉ“en shugaban Æ™asa da na ‘yan majalisar tarayya.

Ana kuma tuhumar ɗan majalisar da laifin kisan wasu mutum uku tare da raunata wasu guda takwas a ƙaramar hukumar Doguwa a lokacin da ake karɓa tare da bayyana sakamakon zaɓen ɗan majalisar.

Kotun tarayyar ta bayar da belinsa bisa wasu sharuÉ—a ciki har da gabatar da manyan sakatarori biyu waÉ—anda suke aiki a gwamnatin jiha da sarki mai daraja ta É—aya da kuma ajiye fasfo É—in sa a kotun.

Mai shari’a Muhammad Yunusa na babbar kotun tarayyar ya ɗage zaman zuwa ranar 22 ga watan Maris ɗin da muke ciki.

A gobe ne aka tsara komawa gaban kotun majisteret ɗin da ta tura shi zuwa gidan yari, don a saurari shawarar da ma’aikatar shari’a ta jihar Kano za ta gabatar game da batun.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haÉ—aka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar Æ´ansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...
X whatsapp