fidelitybank

Dalilin da ya sa muka bayar da belin Doguwa – Baba Jibo

Date:

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke jihar Kano, ta bayar da belin Alhassan Ado Duguwa.

Kakakin kotunan Kano, Baba Jibo Ibrahim, ya ce, hakan ya dace da tsarin shari’a, amma za a ci gaba da sauraron shari’ar zargin kisan kai da ake yi masa.

Ya ce Kotun ta kalubalanci rundunar ‘yan sanda saboda kai Alhassan Doguwa gabanta saboda ba ta da hurumin sauraron irin laifin da ake tuhumarsa da shi.

Yan sandan dai na kuma zargin sa da hannu a harbin wasu mutane da bindiga kwana É—aya bayan kammala jefa Æ™uri’a a mazaÉ“arsa ta Doguwa/Tudun wada a zaÉ“en shugaban Æ™asa da na ‘yan majalisar tarayya.

Ana kuma tuhumar ɗan majalisar da laifin kisan wasu mutum uku tare da raunata wasu guda takwas a ƙaramar hukumar Doguwa a lokacin da ake karɓa tare da bayyana sakamakon zaɓen ɗan majalisar.

Kotun tarayyar ta bayar da belinsa bisa wasu sharuÉ—a ciki har da gabatar da manyan sakatarori biyu waÉ—anda suke aiki a gwamnatin jiha da sarki mai daraja ta É—aya da kuma ajiye fasfo É—in sa a kotun.

Mai shari’a Muhammad Yunusa na babbar kotun tarayyar ya ɗage zaman zuwa ranar 22 ga watan Maris ɗin da muke ciki.

A gobe ne aka tsara komawa gaban kotun majisteret ɗin da ta tura shi zuwa gidan yari, don a saurari shawarar da ma’aikatar shari’a ta jihar Kano za ta gabatar game da batun.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp