fidelitybank

Dalilin da ya sa mu ka dage zaben gwamnoni da na ‘yan majalisu – INEC

Date:

Hukumar Zaɓe INEC, ta ɗage zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokokin jihohi zuwa mako guda, wato zuwa 18 ga watan Maris.

INEC ta tabbatar da ɗage zaɓen, bayan wani taron gaggawa da manyan jami’an hukumar suka yi a Abuja.

A wata sanarwa da ta fitar, wadda ta samu sa hannun jami’in yaɗa labarai da wayar da kai na hukumar, Festus Okoye, ta ce, ta ɗauki matakin ne domin samun damar sanya sabbin bayanai a cikin na’urorin BVAS da za a yi amfani da su a zaɓen mai zuwa.

Sanarwar ta ƙara da cewa shari’ar da jam’iyyun siyasa suka shigar a kotu domin samun izinin duba na’urorin da aka yi amfani da su a zaɓen shugaban ƙasa ne ya kawo jinkiri wurin sauya bayanan da aka yi amfani da su a zaɓen shugaban ƙasa da wanda ake buƙata domin zaɓen gwamnoni.

Wannan na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan wata kotun ɗaukaka ƙara a Najeriya ta amince da buƙatar hukumar zaɓe ta ƙasar ta sake saita na’urar tantance masu zaɓe ta BVAS wadda aka yi amfani da ita a zaɓen shugaban ƙasar.

Tawagar alƙalan kotun mai mutum uku ƙarƙashin jagorancin Joseph Ikyegh ta yanke hukuncin cewa an bai wa INEC damar ne domin gudanar da zaɓen gwamnoni wanda aka tsara gudanarwa a ranar Asabar 11 ga watan Maris tun da fari.

Hukuncin na nufin kotun ta ƙi amincewa da buƙatar da ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar LP Peter Obi ya shigar ta neman hana INEC goge bayanan masu zaɓen da aka naɗa a zaɓen shugaban ƙasar.

Tawagar alƙalan ta ce INEC ta bayyana cewa tana da shirin kwashe bayannan da ke cikin na’urar 176,000 da aka yi amfani da su a zaɓen ta wallafa su a wani rumbun bayananta na daban, ko da yake Obi da LP ba su nuna ƙin amincewa da wannan shiri ba.

uanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...
X whatsapp