Hukumar Zaɓe INEC, ta ɗage zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokokin jihohi zuwa mako guda, wato zuwa 18 ga watan Maris.
INEC ta tabbatar da ɗage zaɓen, bayan wani taron gaggawa da manyan jami’an hukumar suka yi a Abuja.
A wata sanarwa da ta fitar, wadda ta samu sa hannun jami’in yaɗa labarai da wayar da kai na hukumar, Festus Okoye, ta ce, ta ɗauki matakin ne domin samun damar sanya sabbin bayanai a cikin na’urorin BVAS da za a yi amfani da su a zaɓen mai zuwa.
Sanarwar ta ƙara da cewa shari’ar da jam’iyyun siyasa suka shigar a kotu domin samun izinin duba na’urorin da aka yi amfani da su a zaɓen shugaban ƙasa ne ya kawo jinkiri wurin sauya bayanan da aka yi amfani da su a zaɓen shugaban ƙasa da wanda ake buƙata domin zaɓen gwamnoni.
Wannan na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan wata kotun ɗaukaka ƙara a Najeriya ta amince da buƙatar hukumar zaɓe ta ƙasar ta sake saita na’urar tantance masu zaɓe ta BVAS wadda aka yi amfani da ita a zaɓen shugaban ƙasar.
Tawagar alƙalan kotun mai mutum uku ƙarƙashin jagorancin Joseph Ikyegh ta yanke hukuncin cewa an bai wa INEC damar ne domin gudanar da zaɓen gwamnoni wanda aka tsara gudanarwa a ranar Asabar 11 ga watan Maris tun da fari.
Hukuncin na nufin kotun ta ƙi amincewa da buƙatar da ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar LP Peter Obi ya shigar ta neman hana INEC goge bayanan masu zaɓen da aka naɗa a zaɓen shugaban ƙasar.
Tawagar alƙalan ta ce INEC ta bayyana cewa tana da shirin kwashe bayannan da ke cikin na’urar 176,000 da aka yi amfani da su a zaɓen ta wallafa su a wani rumbun bayananta na daban, ko da yake Obi da LP ba su nuna ƙin amincewa da wannan shiri ba.