fidelitybank

Dalilin da ya sa kotu ta ƙwace kujerar NNPP ta baiwa APC a Kano

Date:

Kotun sauraren kararrakin zabe ta Majalisar Dokoki ta kasa da ta Jiha da ke Kano, ta soke zaben Muktar Umar Yerima na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP).

Kotun ta kuma umurci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ta janye takardar shaidar cin zabe da aka baiwa Yerima tun da farko.

Mai shigar da kara, Hafizu Kawu na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ya kalubalanci bayyana Yerima, yana mai cewa bai cancanta ba.

INEC ta ayyana Yerima a matsayin wanda ya lashe zaben majalisar wakilai na mazabar Tarauni.

Sai dai jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, kwamitin mutum uku na kotun karkashin mai shari’a I.P. Chima ya ce, Yerima bai cancanta ba saboda ya yi jabun takardar shedar firamare.

Kotun dai ta ce, kariyar da Yerima ya yi na cewa, ya sauya suna a shekarar 2022, kasancewar yana amfani da sunaye guda uku (Umar Mukhtar Zakari) a fasfo dinsa na kasa da kasa tun a shekarar 2009, yayin da takardar shaidar makarantar firamare ke dauke da Umar Mukhtar.

Har ila yau, makarantar firamare da aka ce, makarantar firamare ta Hausawa, ta yi watsi da takardar shaidar da korarren dan majalisar ya bayar.

Don haka aka ce jam’iyyar NNPP ba ta da dan takara a zaben.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp