Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna, ya bayyana dalilan da suka sa gwamnonin jam’iyyar APC na Arewa suka yanke shawarar marawa mai rike da tutar jam’iyyar, Bola Tinubu baya.
El-Rufai ya bayyana cewa gwamnonin APC na Arewa sun yanke shawarar marawa Tinubu baya domin tabbatar da hadin kai, daidaito da adalci a Najeriya.
Ya bayyana hakan ne a yayin wani taro na gari da wasu kungiyoyin Kiristocin Arewa a Kaduna.
El-Rufai ya ce gwamnonin Arewa sun zauna da Tinubu ne saboda irin rawar da ya taka a lokacin yana Gwamnan Jihar Legas.
A cewar El-Rufai: “A cikin tsarin hadin kai, adalci da adalci a kasar nan, bayan mulkin shugaba Buhari, ya dace a ce fadar shugaban kasa ta tafi Kudu.
“Kuma mun hadu ne a Katsina Lodge kafin Gwamna Aminu Bello Masari ya ce a cikin dukkan ‘yan takarar shugaban kasa, ya kamata mu nemi Ahmed Tinubu saboda irin nasarorin da ya samu a lokacin da yake gwamnan Legas.