fidelitybank

Dalilin da ya sa gwamnati ta janye kudurinta na komawa jami’a

Date:

Fatan dubun dabatar daliban jami’o’i ta kasa ga alama, ya sake dusashewa bayan wata wasikar hukuma ta bayyana cewa gwamnati ta janye umarnin a bude manyan makarantun.

Kungiyar dalibai ta kasa, ta gudanar da jerin zanga-zanga a sassan Najeriya ciki har da rufe harkoki a filin jirgin saman Murtala Mohammed na Lagos, a kokarinta na tilasta janye yajin aikin da malamansu ke yi tsawon watanni.

Gwamnatin dai ta janye umarnin ta na cewa shugabannin jami’o’i su bude manyan makarantun nasu, bayan wani hukunci da kotun ma’aikata ta yi a baya-bayan nan.

A cikin wata wasikar hukuma da aka fitar ranar Litinin, Hukumar kula da Jami’o’i ta Kasa ta nemi shugabanni da ubannin jami’o’i da majalisun gudanarwarsu su bude jami’o’in gwamnatin tarayya bayan rufe su tsawon watanni saboda yajin aikin kungiyar ASUU.

Sai dai, tun kafin dare ya yi, sai Hukumar kula da Jami’o’i ta Kasa ta sake fitar da wata wasikar inda ta ce gwamnati ta janye umarnin da ta bai wa shugabannin jami’o’i tun da farko.

Wasikar wadda ta karade shafukan sada zumunta mai dauke da sa hannun daraktan harkokin kudi da asusun ajiyar Hukumar kula da Jami’o’i, Sam Onazi ta ce “An umarce ni, na janye wasikar Hukumar NUC mai lamba: NUC/ES/138/Vol.64/135, ta ranar 23 ga watan Satumban 2022, game da wannan batu na sama”.

Babu dai wani karin bayani kan dalilin da ya sa gwamnati ta yi amai kuma ta lashe abinta game da wannan umarni na bude jami’o’i.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp