fidelitybank

Dalilin da ya sa ba za mu biya ASUU albashinnsu ba – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Tarayya ta faɗi dalilin da ya sa ba ta biya mambobin ƙungiyar ASUU ta malaman jami’a cikakken albashinsu na watan Oktoba ba, tana mai cewa ba zai yiwu a biya malaman albasahin aikin da ba su yi ba.

Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta ɗauki matakin daina biyan albashin malaman jami’ar na tsawon lokacin da suka ɗauka suna yajin aiki tun daga 14 ga watan Fabarairu zuwa 14 ga Oktoba.

Bayan dawowarsu aikin ne kuma gwamnati ta biya su albashin kwana 17, kamar yadda ASUU ke faɗa, kuma ta yi barazanar ɗaukar mataki.

Hakan ta sa reshen ƙungiyar na Jami’ar Jos ya umarci malaman jami’ar su yi zamansu a gida, duk da cewa ta ce ba yajin aiki suke yi ba.

Cikin wata sanarwa, mai magana da yawun Ma’aikatar Ƙwadago, Olajide Oshundun, ya musanta rahotannin da ke cewa gwamnati ba ta yi wa malaman adalci ba.

“An biya su kuɗin aikin da suka yi ne kawai a Oktoba, daga ranar da suka soke yajin aiki,” a cewar sanarwar.

“An ɗauki matakin ne saboda ba zai yiwu a biya su kuɗin aikin da ba su yi ba. Kowa ta kansa yake yi.”

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp