fidelitybank

Dalilin da ya sa Arewa ta zabi Tinubu – Masari

Date:

Gwamna Aminu Masari na jihar Katsina, ya bayyana dalilin da ya sa shi da wasu gwamnonin Arewa suka goyi bayan aniyar shugaban kasa mai jiran gado, Sen. Bola Tinubu.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a Daura yayin wata ziyarar bankwana da ya kai wa Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruq-Umar.

A cewar sa, gwamnonin Arewa a karkashin jam’iyyar APC sun goyi bayan Tinubu domin mutunta tsarin jam’iyyar na shiyya-shiyya .

Ya kara da cewa: “Allah ya tseratar da mu daga kunya a zaben da ya gabata a kasar nan inda jam’iyyar mu ta All Progressives Congress APC ta samu gagarumar nasara.

“Duk wanda ke kasar nan mai hangen nesa, to ya sake godewa Allah domin da ace jam’iyyarmu ba ta ci zabe ba, mutane na iya tunanin cewa Gwamnatin Tarayya ta gaza ‘yan Najeriya.

“Duk abin da wani ya shirya a kasar nan, Allah ya taimaki Shugaba Muhammad Buhari ya kare mutuncin sa, domin da a ce mun fadi zabe, da shi ne aka fara zargi.

“Masu hangen nesa sun ga haka, musamman mu gwamnonin da suka fito daga Arewa a karkashin jam’iyyar APC. Mun ga yunkurin bata sunan Buhari.

“Kowa ya san cewa duk jam’iyyun siyasa sun yi imani da tsarin yanki, amma wasu mutane a jam’iyyarmu sun so a ajiye hakan a gefe, amma mun yi watsi da yunkurinsu.”

A cewar Masari, rashin mutunta tsarin shiyya-shiyya da wasu jam’iyyun adawa suka yi ne ya sanya su cikin rigingimun da ke tada su.

“Don haka, da mun yi haka, Allah ne kadai zai san halin da kasar ke ciki a halin yanzu. Saboda haka, dole ne mu ci gaba da cika alkawuranmu.

“Shi ya sa ‘yan Arewa suka yi nasara a lokacin suka kuma samu mutunta mutanenmu, domin da zarar mun ce eh, eh kullum ne,” in ji shi.

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp