Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, ya bayyana dalilin da ya sa wakilan jam’iyyar APC na kasa a shiyyar Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas, na zaben fidda gwanin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, suka zabi Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a maimakon tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi da Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo.
A cewar El-Rufai, gwamnonin yankin Arewa maso Yamma sun gana inda suka yanke shawarar cewa, Tinubu, wanda shi ne jagoran jam’iyyar APC na kasa, shi ne wanda ya fi sayar da shi a cikin ‘yan Kudu biyar da suka mika wa shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Sannan kuma, shugaba Buhari ya ki zabar wani dan takara a cikin biyar din, ya kuma dage cewa, ya bukaci gwamnonin da su bar wakilai su yanke shawara, in ji El-Rufai.
A zaben fidda gwani na takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, tsohon gwamnan jihar Legas, Tinubu ne ya samu kuri’u 1,271 inda ya doke abokin hamayyarsa Amaechi wanda ya samu kuri’u 316 yayin da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya zo na uku a zaben fidda gwanin da ya samu kuri’u 235.
Kuma El-Rufai ya ce haka ne saboda gwamnonin yankin Arewa maso Yamma sun yanke shawarar cewa, Tinubu ne ya fi dacewa kuma Arewa maso Gabas ma sun bi. A cewar Daily Post.
“Ba zan iya cewa, dukkanmu mun makale da Bola Tinubu ba. Ba dukkanmu muka makale da Bola Tinubu ba. A yawancin jihohinmu, an raba kuri’un wakilan. Kuma na je na yi wa wakilan Kaduna jawabi na karshe kafin a kada kuri’a.
“Ban san yadda wakilan suka kada kuri’a ba, amma ra’ayin da na samu bayan zaben shi ne yawancinsu sun zabi Asiwaju, wasu sun zabi Amaechi wasu kuma suka zabi mataimakin shugaban kasa, Osinbajo.