fidelitybank

Dalilin da ya sa aka tsige mataimakin gwamnan Edo

Date:

Majalisar dokokin jihar Edo ta tsige mataimakin gwamnan jihar Philip Shaibu.

Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito an tsige Shaibu a zaman da majalisar ta yi ranar Litinin a Benin, babban birnin Edo.

Tsige Shaibu ya biyo amincewa da wani rahoton kwamitin mutum bakwai da alƙalin alƙalan jihar Daniel Okungbowa ya kafa domin yin bincike kan zarge-zargen aikata ba daidai ba da ake yi wa mataimakin gwamnan.

A makon da ya gabata ne majalisar dokokin jihar ta Edo ta fara shirin tsige Shaibu. Ƴan majalisa 21 cikin 24 ne suka sa hannu kan takardar ƙorafin.

Sun zargi Shaibu da yin ƙarya da kuma bayyana sirrikan gwamnatin jihar.

A zaman da ta yi ranar Talatar da ta gabata, shugaban majalisar, Blessing Agbebaku ya shaida wa ƴan majalisa cewa wa’adin kwana bakwai da aka bai wa Shaibu ya mayar da martani ga takardar fara shirin tsige shi ya wuce.

Tsige Shaibu na da nasaba da takun saƙar siyasa da ke tsakaninsa da ubangidansa Godwin Obaseki.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp