fidelitybank

Dalilin da ya sa a ka aiyana ƴan fashin daji a matsayin ƴan ta’adda — Osinbajo

Date:

 

 

 

 

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya ce dalilin da ya sa gwamnatin tarayya ta aiyana ‘yan fashin daji a matsayin ƴan ta’adda a hukumance shi ne don baiwa jami’an tsaro damar ɗaukar tsauraran matakai a kansu.

Mataimakin shugaban ƙasan ya baiyana haka ne a fadar Sarkin Katsina a ranar Asabar domin yin ta’aziyya ga Dahiru Barau Mangal, wanda ya rasa mahaifiyarsa, Hajiya Murja.

Osinbajo ya kuma baiyana fatansa na cewa dukkan sabbin matakan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarta sun sanya ya kamata a iya ganin sauyi mai ma’ana sosai a harkar tsaron Nijeriya.

Yayin da yake mika godiyarsa ga Sarkin Katsina da sarakunan sa bisa kyakkyawar tarba da aka yi masa, Osinbajo ya yi addu’ar Allah ya ba wa masarautarsa ​​da ƙasa baki daya zaman lafiya.

Ya baiyana ƙwarin gwiwa ce za a samu wadata da farin ciki da kuma zaman lafiya a ƙasar nan kafin wa’adin mulkinsu ya ƙare.

Da yake mayar da martani, Sarkin Katsina, ya bayyana farin cikinsa da ayyana ‘yan bindiga a matsayin ‘yan ta’adda a hukumance.

 

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...

Buhari ya ban umarni na kula da Talakawan Najeriya – Peter Obi

Jagorar jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya ce,...

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...
X whatsapp