Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya ce, ya zare ɗansa daga makarantar gwamnati ne saboda barazanar kai hari da garkuwa.
El-Rufa’i, ya ce, ya ɗauki matakin sa ɗansa a makarantar ne, domin tabbatar da kwarin guiwarsa ga tsarin ilimin Kaduna, kamar yadda Punch ta rawaito.
Malam Nasiru ya yi wannan zancen ne a wurin taron manema labarai da ake shirya wa ministoci a fadar shugaban ƙasa dake Abuja, ranar Alhamis.
Ya bayyana cewa, shekaru biyar baya tun zuwansa kan mulki, gwamnatinsa ta ɗauki malaman makaranta fiye da adadin waɗan da ta kora daga aiki.
Gwamnan ya ce: “Mun kori Malamai 22,000 kuma mun ɗauki 25,000. Mun gwada su lokuta da dama, wasu su faɗi kuma su sake faɗuwa, za mu kore su mu ɗauki wasu sabbi.” “Mun shirya inganta nagartan Malamai, saboda Malami shi ne ilimin ba wai ajin da ake zama ba. Yanzu zamu kawar da wasu malaman Sakandire. Amma mun ɗauki malaman da zasu koyar a Sakandire 7,700, muna jira ne mu kammala sallamar waɗan can. Kuma jami’an gwamnati mun cimma matsaya zamu saka ‘ya’yan mu a makarantun gwamnati.”