fidelitybank

Dalilan da ya sanya El-Rufa’i ya zare dansa daga makarantar gwamnati

Date:

Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya ce, ya zare ɗansa daga makarantar gwamnati ne saboda barazanar kai hari da garkuwa.

El-Rufa’i, ya ce, ya ɗauki matakin sa ɗansa a makarantar ne, domin tabbatar da kwarin guiwarsa ga tsarin ilimin Kaduna, kamar yadda Punch ta rawaito.

Malam Nasiru ya yi wannan zancen ne a wurin taron manema labarai da ake shirya wa ministoci a fadar shugaban ƙasa dake Abuja, ranar Alhamis.

Ya bayyana cewa, shekaru biyar baya tun zuwansa kan mulki, gwamnatinsa ta ɗauki malaman makaranta fiye da adadin waɗan da ta kora daga aiki.

Gwamnan ya ce: “Mun kori Malamai 22,000 kuma mun ɗauki 25,000. Mun gwada su lokuta da dama, wasu su faɗi kuma su sake faɗuwa, za mu kore su mu ɗauki wasu sabbi.” “Mun shirya inganta nagartan Malamai, saboda Malami shi ne ilimin ba wai ajin da ake zama ba. Yanzu zamu kawar da wasu malaman Sakandire. Amma mun ɗauki malaman da zasu koyar a Sakandire 7,700, muna jira ne mu kammala sallamar waɗan can. Kuma jami’an gwamnati mun cimma matsaya zamu saka ‘ya’yan mu a makarantun gwamnati.” 

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp