fidelitybank

Dalilan da ya sanya ƴan takara ke rububin Wike

Date:

Alamu na nuna cewa gwamnan jihar Rivers Nyesom Wike ya zama allurar cikin ruwa, wanda ‘yan Magana kan ce mai rabo ka dauka sakamakon yadda ‘yan takarar shugaban kasa na manyan jam`iyyun siyasar Najeriya ke ribibin jan sa a jika.

Ko a makon da ya wuce ɗan takaran jam`iyyar APC Bola Tinubu da na Labour, Peter Obi da kuma na PDP Atiku Abubakar sun gana da Wiken a London.

Wasu makwannin da suka wuce ma ɗan takaran shugaban kasa na jam`iyyar NNPP Rabi’u Musa Kwankwaso ya kai masa irin wannan ziyarar zawarcin.

Ko me ya sa ake wannan kokuwar a kan sa? Dr Abubukar Kari masanin siyasa ne a jami`ar Abuja, kuma ya shaidawa BBC cewa gwamna ne na wata jiha mai dimbin jama’a da ke kusan mataki na 7 a yawan masu kaɗa kuri’a.

Sannan a sashin kudu maso kudancin Najeriya babu hamshaƙin ɗan siyasa irinsa, sannan ya na da karfin faɗa a ji tsakanin wasu hamshaƙan ‘yan siyasa a jihohi da masu arziki.

Wannan na daga cikin dalilin da ya sa ‘yan siyasa ke ganin idan suka yi zawarcinsa zai ba su tagomashi a takararsu.

Sai dai masanin na cewa da wuya ya iya barin PDP, ganin cewa ya gina kasan a jam’iyyar, sannan yana da manyan yara da ya gina yanzu haka suke takara.

Babu shaka a cewar masanin Wike na iya yiwa jam’iyyar PDP zagon-kasa, wannan shi ne dalilin da ya sa ake zawarcinsa, sannan ɗan takarar shugabanci kasa na PDPn Atiku Abubakar ke son sulhu da shi.

Masanin ya ce babu taƙamaimai abin da za a iya cewa ga shi abin da yake so, sai dai yana son ƙara karfinsa ne na faɗa aji.

Amma a cewar masanan idan mulki ya fita daga hannunsu karfin faɗa ajinsa zai ragu, dalilin da ya sa ya ke son sake gina tagomashinsa kenan kafin zaɓen 2023.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp