Tsohon shugaban kasar Najeriya a mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, ya bayyana dalilin da ya sa bai kara aure ba, tun bayan rasuwar tsohuwar matarsa, Maryam Babangida, wadda ta rasu a ranar 27 ga watan Disamban 2009.
Yayin wata tattaunawa da talabijin ta Trust TV da ya yi, Ibrahim Badamasi Babangida, ya ce, “Na zaÉ“i yin hakan ne, domin na martaba ta”.
Kwanan baya dai an yi ta raÉ—e-raÉ—in cewa, tsohon shugaban na shirin yin wani auren, domin samun abokiyar zama, amma yayin wannan tattaunawa ya ce,”Sam ba gaskiya bane”.
“Haba da na yi aure da kun fi kowa sani, saboda haka ban yi aure ba, ra’ayi na ne kuma wannan’’ in ji IBB.