fidelitybank

Dalilan da ya sa na keson kujerar Buhari – Osibanjo

Date:

Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya ce, inganta ilimi ga matasa da samar da ayyukan yi na daga cikin dalilan da suka sanya shi shiga takarar shugaban kasa a 2023.

Osinbajo ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga Sarkin Bauchi Alhaji Rilwanu Sulaimanu a ranar Talata a fadarsa da ke Bauchi.

Mataimakin shugaban kasar ya je jihar ne a wani bangare na tuntubar sa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), gabanin zaben shugaban kasa na 2023.

Damuwarmu a matsayinmu na gwamnati ita ce ta yadda za a bai wa talaka dama don a yi masa aiki da kuma samun rayuwa mai inganci wanda shi ya sa aka yi ayyuka da dama da muka gudanar, musamman shirin zuba jari na zamantakewa. don kyautata yawan jama’a.

Amma kuma, mun damu da matasa; ta yaya za mu inganta ba wai kawai ingancin ilimin matasa ba, har ma da damar da matasa za su iya samun ayyukan yi, a yi musu aiki. Kuma wannan na iya bayyana dalilin da ya sa nake tsayawa takarar shugabancin kasar nan a 2023.

“Na taba zama mataimakin shugaban kasa Muhammadu Buhari tsawon shekaru bakwai kuma Allah ya taimake ni, zan cika wannan wa’adin nan da Mayu 2023,” inji shi.

Osinbajo ya kara da cewa: “Kuma a wannan matsayi, kamar yadda mai martaba sarki zai sani, an baje ni wajen gudanar da mulki a mataki na koli, godiya ta tabbata ga yadda shugaban kasa ya yi gaskiya da rikon amana kuma na koyi abubuwa da dama.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...
X whatsapp