fidelitybank

Dalilan da ya sa APC ta lashe zaɓen Imo da Kogi – Uzodinma

Date:

Gwamna Hope Uzodinma na jihar Imo ya bayyana cewa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta yi nasara a jihar sa da kuma Kogi a zaben gwamna, saboda yadda jam’iyyar ta samu karbuwa.

Uzodinma ya dage cewa ‘yan Najeriya na farin ciki da jam’iyyar All Progressives Congress, APC, sakamakon tasirin shugaba Bola Tinubu.

A Imo, Uzodinma ya sake lashe zabensa bayan ya doke abokan takararsa na jam’iyyar PDP da kuma Labour Party.

Dan takarar APC, Usman Ododo shi ma ya yi nasara a jihar Kogi, amma PDP ta yi nasara a jihar Bayelsa inda aka sake zaben Gwamna Douye Diri.

Uzodinma da Ododo sun ziyarci Tinubu a fadar shugaban kasa ta Villa inda suka ba shi takardar shaidar dawowar su.

Da yake jawabi yayin ziyarar, Uzodinma ya ce nasarar da jam’iyyar APC ta samu a jihohin Kogi da Imo ya nuna “karuwar farin jinin” jam’iyyar.

A cewar Uzodinma: “Kun tuna cewa zaben ranar 11 ga watan Nuwamba, babbar jam’iyyar mu ta APC, na kara samun karbuwa kuma ta fito cikin nasara a jihohin Kogi da Imo.

“Nasarar da muka samu a zaben ya nuna cewa har yanzu ’yan Najeriya na farin ciki da jam’iyyar APC. ‘Yan Najeriya sun kada kuri’a ga shugaban kasa kuma wannan nasara ta tabbatar da wannan ikirarin ta hanyar masu kada kuri’a a jihar Kogi da Imo.

“Don haka mun zo ne domin mu karrama shugaban kasa sannan kuma mu yi amfani da damar mu yi masa godiya bisa goyon bayansa da shawarwarinsa da kuma hikimarsa.

“Ya ba mu damar da kuma nasarorin da ya samu tun lokacin da ya zama shugaban kasa wanda yawancin mu ke amfani da shi don samun damar shawo kan masu jefa kuri’a su zabe mu.”

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp