An tsinci gawar wani dalibin babbar Sakandire na aji 2 na makarantar Owena Community Grammar School, Owena, a karamar hukumar Ondo ta Gabas a jihar Ondo, Mwafor Emmanuel, a cikin kogi.
Rahotanni sun ce, dalibin mai shekaru 19 ya nutse a cikin wani kogi da ke bayan makarantarsa.
Wani malami a makarantar, wanda ya yi magana cikin aminci ya ce: “Lamarin ya faru ne bayan sa’o’in makaranta. Sauran dalibai sun tafi gidajensu lokacin da yaron ya yanke shawarar tafiya ya yi iyo shi kadai. Ya cire rigarsa da takalminsa kafin ya yi tsalle ya shiga cikin kogin. Tabbas ya nutse lokacin da ya zurfafa cikin kogin.
“Abin takaici, watakila an ceto shi idan wasu dalibai na tare da shi a lokacin da lamarin ya faru. Da sun ɗaga ƙararrawa. Amma ya tafi shi kaɗai don yin iyo.”
An gayyaci jami’an binciken ‘yan sanda washe gari lokacin da wani mai wucewa ya gano gawarsa aka ajiye shi a babban asibitin jihar da ke cikin garin Ondo.
Da take tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Funmi Odunlami, ta bayyana rasuwar a matsayin abin takaici.