fidelitybank

Daliban Sokoto dake karatu a Ukraine na cikin firgici – Tambuwal

Date:

Wasu ɗaliban Najeriya ƴan asalin jihar Sokoto da rikicin Rasha ya rutsa da su a Ukraine, sun yi kira ga gwamnatin jihar da ta gaggauta kwashe su, domin suna ganin daman barin ƙasar zai gagara nan ba da dadewa ba idan lamarin ya tsananta.

Ɗaliban da aka bayyana guda 22 sun yi wannan kiran ne a zantawar da gwamnan Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya haɗa ta kafar zoom da su tare da kuma iyayensu daga gidan gwamnatin jihar.

Sanarwar da gwamnatin jihar ta fitar ta ce, ɗaya daga cikin ɗaliban mai suna, Aisha Kabir ta shaida wa gwamnan cewa, halin da ake ciki a Kharkiv ya tsananta.

Rahotanni a safiyar Lahadi sun ce, sojojin Rasha sun kutsa Kharkiv, kuma ana gwabza faɗa a birnin na biyu mafi girma a Rasha.

“Muna jin ƙarar harbe-harbe, ko da yake ana ƙoƙarin tafiya da mu cikin bus zuwa Romania, amma direbobin suna jin tsoron za a iya kai masu hari, muna ganin jirgin ƙasa ne ba ya da hatsari wanda za mu yi sauƙin ficewa.” In ji ɗalibar kamar yadda sanarwar da mai magana da yawun gwamnan Muhammad Bello ya fitar ta bayyana.

Wani ɗalibin kuma Shuaibu Muhammad, ya ce, suna fuskantar ƙalubale a Krakow na Poland domin ba isasshen abinci da wurin bacci mai kyau. “Daga Lviv zuwa Krakow tafiyar awa 12 ce, kuma yawancinmu ba mu san kowa ba da za mu yi magana da shi lokacin da muka iso.

Wasu sun c,e suna fuskantar ƙalubale na yanayin sanyi da rashin tufafin da ya dace da bargon bacci.

Wata ɗaliba Zarah Ibrahimn ta bayyana fargabar cewa “ta ji ana faɗi daga gobe za a hana wa ƴan ƙasashen waje fita Lviv, ta na mai jaddada cewa Kharkiv na tattare da hatsari”

A nasa ɓangaren gwamnan jihar ya yi wa ɗaliban alƙawalin cewa da su da sauran ɗalibai ƴan Najeriya za su fice daga Ukraine nan ba da dadewa ba kuma su dawo gida lafiya.

Gwamnan ya ce ya ba ma’aikatar kuɗi ta jihar umarnin ta tura wa ɗaliban da ke cikin mawuyacin hali tallafin kudi kimanin dala 200 zuwa 300.

Iyayen ɗaliban sun yaba kan yadda gwamnatin Sokoto ta nuna damuwarta da kuma tausayin ƴaƴansu tare da jan hankalin ƴaƴansu da su yi taka-tsan-tsan a yayin ficewa Ukraine. In ji BBC.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp