fidelitybank

Daliban Najeriya 2,500 sun makale a jami’ar Sudan – SOSAN

Date:

Kungiyar tsofaffin daliban kasar Sudan ta Najeriya, SOSAN, ta yi gargadin cewa sama da daliban Najeriya 2,500 da ba su da takardun karatu sun makale a jami’ar Sudan/African University ba tare da abinci ko ruwa da kudi ba.

Da yake jawabi jim kadan bayan gabatar da addu’o’i na musamman domin kare lafiyar daliban, shugaban kungiyar, Aliyu Abdulkadir Abdulkadir ya ce, sun samu kiraye-kirayen nuna damuwa daga daliban cewa rayuwarsu na cikin hadari matuka.

Ya ce kamar yadda yake a yanzu, hatta dalibai 5,000 da aka ce an kai su Masar har yanzu suna kan iyaka domin ba a ba su izinin shiga kasar ba, yayin da wasu direbobin bas din suka jefa su cikin daji saboda rashin biyan kudadensu.

Abdulkadir ya koka da yadda hatta kudaden da aka ce an ware domin kwashe daliban ana tafka ta’asa, wanda hakan ya sanya daruruwan daliban cikin mawuyacin hali a cikin birnin Khartoum.

Ya ce, “Rahotanni da ke zuwa mana sun nuna cewa a yanzu haka duk da cewa ba a samu asarar rayuka ba, amma an ce an yi wa wasu dalibai mata fyade yayin da fadan bindiga ya kai a cikin jami’ar”.

Wani tsohon dalibin jami’ar Sudan Gambo Ado, ya ce har yanzu suna da dalibai a jami’ar Sudan International University of Africa da ke makale. Ya ce yawancin mata ne kuma ba su da abinci ko matsuguni.

Ya ce tuni sun kai rahoto ga gwamnati lamarin daliban da ba su da takardun karatu.

“A yanzu babu wata murya daya da ke magana da daliban Najeriya, kudaden da aka aika musu ba su kai gare su ba, kuma galibinsu sun aika da faifan bidiyo a cikin daji suna ihun neman taimako,” inji shi.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp