fidelitybank

Dalibai za su fara cin gajiyar bashin miliyan 1.2 – Tinubu

Date:

Akalla matasa miliyan 1.2 ne za su fara cin gajiyar shirin bai wa ɗalibai bashin karatu da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta ɓullo da shi.

Ana sa ran tsarin shiga cikin shirin, wanda Shugaba Tinubu ya amince da shi a ranar 3 ga Afrilu, zai fara “nan ba da jimawa ba,” kamar yadda Akintunde Sawyer, Manajan Darakta da kuma Babban Jami’in Gudanarwa na Asusun ba da bashi na Ilimi na Najeriya (NELFUND) ya bayyana.

A ƙarkashin wannan shiri, kashi ɗaya cikin dari na kuɗaden shiga na shekara-shekara na Hukumar Tara Haraji ta Kasa (FIRS) za ta ɗauki nauyin shirin.

Tare da shirin samun kudin shiga na Naira tiriliyan 19.4 da aka ware wa FIRS a bana, za a iya ware makudan Naira biliyan 194 a matsayin bashin da za a baiwa daliban da suka cancanta.

Sharuɗɗan biyan bashin sun nuna cewa za a fara biyan bashin shekaru biyu bayan kammala aikin yi wa kasa hidima (NYSC).

Sawyer ya zayyana tsarin rajistar, wanda ya nuna cewa wadanda za su ci gajiyar shirin za su bukaci bayar da lambar jarabawarsu ta JAMB, da Lambar Shaida ta Kasa (NIN), da Lambar Tabbatar da Banki (BVN) don neman rancen.

Bugu da ƙari, ɗaliban da suke neman rancen dole ne su ba da cikakkun bayanan karatun su.

“Ga wadanda suka yi nasara samun rancen, za mu biya cikakken adadin kuɗaɗen makarantarsu kai tsaye ga jami’o’in da suke karatu.”

“Haka kuma za a biya daidaikun mutane alawus na amfanin yau da kullum don kula da kansu ta yadda za su iya yin abubuwan.”

“Za su iya amfani da alawus ɗin don tabbatar da cewa akwai isassun dama a gare su don tsira daga wahalar da ɗalibai ke fuskanta.”

Burin Shugaba Tinubu game da shirin ya kunshi kuma yana da nufin fadada hanyoyin ilimi ga ‘yan Najeriya da dama.

Kamar yadda Sawyer ya jaddada, an tsara shirin ne don samun damar shiga da kuma tabbatar da cewa ɗalibai daga sassa daban-daban za su iya cin gajiyar damar samun yin karatu.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp