fidelitybank

Dalibai za su fara cin gajiyar bashin miliyan 1.2 – Tinubu

Date:

Akalla matasa miliyan 1.2 ne za su fara cin gajiyar shirin bai wa ɗalibai bashin karatu da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta ɓullo da shi.

Ana sa ran tsarin shiga cikin shirin, wanda Shugaba Tinubu ya amince da shi a ranar 3 ga Afrilu, zai fara “nan ba da jimawa ba,” kamar yadda Akintunde Sawyer, Manajan Darakta da kuma Babban Jami’in Gudanarwa na Asusun ba da bashi na Ilimi na Najeriya (NELFUND) ya bayyana.

A ƙarkashin wannan shiri, kashi ɗaya cikin dari na kuɗaden shiga na shekara-shekara na Hukumar Tara Haraji ta Kasa (FIRS) za ta ɗauki nauyin shirin.

Tare da shirin samun kudin shiga na Naira tiriliyan 19.4 da aka ware wa FIRS a bana, za a iya ware makudan Naira biliyan 194 a matsayin bashin da za a baiwa daliban da suka cancanta.

Sharuɗɗan biyan bashin sun nuna cewa za a fara biyan bashin shekaru biyu bayan kammala aikin yi wa kasa hidima (NYSC).

Sawyer ya zayyana tsarin rajistar, wanda ya nuna cewa wadanda za su ci gajiyar shirin za su bukaci bayar da lambar jarabawarsu ta JAMB, da Lambar Shaida ta Kasa (NIN), da Lambar Tabbatar da Banki (BVN) don neman rancen.

Bugu da ƙari, ɗaliban da suke neman rancen dole ne su ba da cikakkun bayanan karatun su.

“Ga wadanda suka yi nasara samun rancen, za mu biya cikakken adadin kuɗaɗen makarantarsu kai tsaye ga jami’o’in da suke karatu.”

“Haka kuma za a biya daidaikun mutane alawus na amfanin yau da kullum don kula da kansu ta yadda za su iya yin abubuwan.”

“Za su iya amfani da alawus ɗin don tabbatar da cewa akwai isassun dama a gare su don tsira daga wahalar da ɗalibai ke fuskanta.”

Burin Shugaba Tinubu game da shirin ya kunshi kuma yana da nufin fadada hanyoyin ilimi ga ‘yan Najeriya da dama.

Kamar yadda Sawyer ya jaddada, an tsara shirin ne don samun damar shiga da kuma tabbatar da cewa ɗalibai daga sassa daban-daban za su iya cin gajiyar damar samun yin karatu.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp