fidelitybank

Dalibai sun yi zanga-zanga a kan harbe dan uwansu da Amotekun suka yi

Date:

Daliban Rufus Giwa Polytechnic dake Owo, a Jihar Ondo a ranar Juma’a sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da rasuwar abokin su, Folarera Ademola.

Wani jami’in Amotekun Corps ne ya kashe Ademola, dalibin ND1 daga sashen fasahar dakin gwaje-gwaje na kimiyya.

Bayan faruwar lamarin, daliban da suka yi zanga-zangar sun baiwa gwamnatin jihar wa’adin sa’o’i 24.

Daliban sun bukaci da a mika jami’in Amotekun da ya yi harbin ga hukumar ‘yan sanda, domin daukar matakin shari’a, da shirya yadda za a binne marigayin, da kuma biyan diyya ga iyalansa.

An ce an harbe dalibin ne a ranar 27 ga watan Yuni, a kofar gidan iyayensa, a cewar Olorunda Oluwafemi, shugabar kungiyar daliban.

Marigayin, a cewar Oluwafemi, ya jure raunin harbin da ya samu na tsawon kwanaki goma kafin a kai shi cibiyar kula da lafiya ta tarayya dake Owo, inda ya bar fatalwar ranar Alhamis.

Oluwafemi ya dage cewa, daliban da suka yi zanga-zangar za su zarce daga kofar makarantar zuwa fadar Olowo kafin su ci gaba da zanga-zangar zuwa ofishin Amotekun don kara bayyana kokensu.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp