Wasu ƙarin ‘yan Najeriya 125 sun isa Abuja daga Sudan.
Mutanen waɗanda jirgin Tarco B737-300 ya ɗauko daga Port Sudan sun sauka a filin jirgin saman Abuja da tsakar ranar Asabar.
A yanzu adadin ‘yan ƙasar da aka kwaso daga Sudan ya kai 2,371.
Jami’an shige da fice da na hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasar NEMA, da jami’an hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta ƙasar ne suka tarbe su a filin jirgin.
A ranar uku ga watan Mayu ne jirgin farko ɗauke da ‘yan ƙasar daga Sudan ya sauka a filin jirgin Abuja.
Tun daga ranar ne kuma ake ta jigilar ƙwasar ɗaliban ƙasar waɗanda suka maƙale a ƙasar sakamakon faɗan da ya ɓarke tsakanin sojojin ƙasar da dakarun RSF masu sanye da kayan sarki.