fidelitybank

Dala biliyan 49.8 ba su ɓace a zamani na ba – Jonathan

Date:

Tsohon shugaban ƙasar Najeriya Goodluck Jonathan ya ce dala biliyan 49.8 ba ta ɓace ba a zamanin mulkinsa kamar yadda tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Sanusi Lamiɗo Sanusi ya bayyana a 2014.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa Jonathan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a Abuja a wajen ƙaddamar da wani littafi a Abuja.

Tsohon shugaban ƙasar ya ce ba zai yiwu maƙudan kuɗaɗe irin wannan sun ɓace a wata ƙasa, amma kuma ta iya ci gaba da biyan albashi.

“Ina ganin akwai buƙatar in amsa wasu maganganu da ya faɗa a cikin littafin, musamman waɗanda suke da alaƙa da ni.

“Ya ce an cire shi ne saboda fitar da maganar da ya yi a kan ɓacewar kuɗi dala biliyan 49.8 daga lalitar gwamnati. Gaskiya wannan ba haka ba ne. Ba cire shi aka yi ba, dakatar da shi aka yi,” in ji shi.

“Kafin mu gama kuma wa’adinsa ya ƙare, wataƙila da mun dawo da shi. Amma har yanzu ban yarda cewa dala biliyan 49.8 ya ɓace ba.”

Jonathan ya ƙara da cewa bayan binciken ƙwaƙwaf da aka yi, “da rahoton ya fito, dala biliyan 1.48 ne rahoton ya ce ba a tabbatar ba, amma nan ma sai aka buƙaci kamfanin NNPC ya biya kuɗin a asusun gwamnatin tarayya.”

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp