Ƴar majalisar Dattawan Najeriya mai wakiltar Kogi ta tsakiya da mambobin majalisar suka dakatar, Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ta bayyana dakatarwar da aka yi mata a matsayin ‘zalunci’
A ranar Laraba ne majalisar ta amince da dakatar da Sanata Natasha na tsawon wata shida saboda zargin ”saɓa ƙa’idar aiki” bayan saɓanin da ya shiga tsakaninta shugaban majalisar dattawan, Sanata Godswill Akpabio.
Cikin wani saƙo da ta wallafa a shafinta na Facebook, Sanata Natasha ta yi zargin cewa dakatarwar da aka yi mata ba a bi ƙa’ida ba, kuma an yi haan ne domin a rufe mata baki.
”Dakatarwar da aka yi min ba bisa ƙa’ida ba ta ci karo da dokokin adalci, kuma hakan ba zai hanani ci gaba a hidimta wa al’ummar da nake wakilta ba”, a cewarta
Da farko dai saɓanin ya fara ne da sauya wa ƴar majalisar wurin zama a zauren, kafin daga baya ta zarge shi da yunƙurin cin zarafinta ta hanyar lalata.