Dakarun sojin sama na Operation Thunder Strike ta murkushe ‘yan bindiga kusan 20 a babban yankin makarantar horas da sojoji ta Najeriya (NDA), Kaduna.
Politics Nigeria ta rawito cewa, an ga ‘yan ta’addan da ke tafiya cikin babura kusan 50 a yammacin ranar Alhamis. Amma sun gamu da ruwan wuta, yayin da aka aike da jirage masu saukar ungulu guda biyu na rundunar sojojin saman Najeriya, domin su dakile su.
Idan ba a manta ba, a watan Yunin 2021 ne ‘yan bindiga suka kai farmaki NDA suka yi awon gaba da wani Manjo na Sojan Najeriya suka harbe sojoji biyu har lahira.
’Yan ta’addan dauke da muggan makamai wadanda suka addabi yankunan karkarar Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabashin Najeriya, suna kashe-kashe, garkuwa da mutane, suna tilastawa mutane barin gidajensu, tare da yi wa hukuma barazana.