fidelitybank

Dakarun Soji sun kama makamai a Tafkin Chadi

Date:

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa (MNJTF) da ke aiki a yankin tafkin Chadi sun fatattaki wasu ‘yan ta’adda tare da kwato manyan makamai.

A wata sanarwa da kakakin rundunar MNJTF, Laftanal Kanal Kamarudeen Adegoke, ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata, ya ce an samu nasarorin baya-bayan nan ne a sakamakon sabon farmakin da aka kai wa ‘yan ta’adda, mai suna “Operation Harbin Kunama, (Scorpion sting)”.

“Ayyukan da sojojin na MNJTF ke ci gaba da yi ya kara rage karfin ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP wajen gudanar da ayyukansu a yankin tafkin Chadi.

“Tsarin kai hari da kaurin sojojin na MNJTF ya ci gaba da haifar da sakamako mai ban mamaki.

“Bayan wani hari da ‘yan ta’addar BH/ISWAP suka kai wa sojoji a yankin Arege, wanda aka samu nasarar dakile shi, sojojin rundunar sun yi amfani da karfin tuwo a ranar 11 ga watan Mayu a yankin gaba daya.

Sanarwar ta kara da cewa, an kwato abubuwa da dama da suka hada da bindigar Dushka guda daya, Dushka Turrell da wata motar bindiga da ta kone yayin da aka kashe ‘yan ta’adda da dama yayin arangamar.

Sanarwar ta ce an yi nasarar gudanar da aikin share fage a yankin Ferondiya da ke yankin tafkin Chadi wajen fatattakar ‘yan ta’adda.

Sanarwar ta ce, kayan aikin da aka kwato daga hannun ‘yan ta’addan sun hada da manyan motocin bindiga guda biyu, bindigogin Anti – Aircraft guda biyu, bututun RPG daya, bindigogin AK 47 guda biyu, bam RPG daya da kuma tayoyin motar kirar Toyota Buffalo guda uku.

Sauran su ne zagaye 387 na 12.7mm, 440 na 7.62mm x 54mm da 364 na 7.62mm x 50 mm harsashi.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp