fidelitybank

Dagogo ya shaƙi iskar ƴanci a jihar Ribas

Date:

An saki Farah Dagogo, dan takarar gwamna a jam’iyyar PDP a jihar Ribas, kuma dan majalisar wakilai mai ci, bayan shafe kusan wata guda yana tsare.

Hakan ya biyo bayan hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Fatakwal karkashin jagorancin mai shari’a E A. Obile ta yanke hukuncin sakin Dagogo daga gidan yari na Fatakwal a ranar Litinin.

Wannan umarni ya biyo bayan wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umurci jam’iyyar PDP da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da su gabatar da hujja a ranar 24 ga watan Mayu da ya sa ba za a amince da bukatar da dan majalisar tarayya ya gabatar a kan mutanen biyu da ake kara a zaben fidda gwani na gwamnan jihar.

A bisa umarnin Mai shari’a Obile, an kai Dagogo kotu a keken guragu.

Mai shari’a Obile ya bayar da sammaci ga mahukuntan gidan gyaran hali, inda ya umarce shi (Dagogo) da ya gurfana a gaban kotu kuma a bayar da belinsa bisa ga umarnin da aka bayar.

Sai dai an mayar da Dagogo gidan yari a hanyar Dockyard Road da ke tsohuwar unguwar Fatakwal da jami’an ’yan sanda suka yi, domin kammala duk wasu tsare-tsaren belin da ake sa ran kammalawa nan ba da jimawa ba.

A halin da ake ciki, lauyan Dagogo, Dakta Innocent Ekwu, ya yi barazanar shigar da karar kotu a kan dukkan hukumomi idan aka saba wa umarnin kotun.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp